7. Zan shirya waɗanda za su hallakata.Kowannensu da makamansa,Za su sassare zaɓaɓɓun itatuwanal'ul ɗinta, a jefa su a wuta.
8. “Al'ummai masu yawa za su wuce ta gefen wannan birni, kowane mutum zai ce wa maƙwabcinsa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan babban birni?’
9. Za su amsa, su ce, ‘Domin sun keta alkawarin Ubangiji Allahnsu, suka yi sujada ga gumaka, suka bauta musu.’ ”
10. Ku mutanen Yahuza, kada ku yikuka saboda sarki Yosiya,Kada ku yi makokin rasuwarsa,Amma ku yi kuka ƙwarai sabodaɗansa Yehowahaz.Sun ɗauke shi, sun tafi da shi, ba zaiƙara komowa ba,Ba kuma zai ƙara ganin ƙasar daaka haife shi ba.
11. Gama haka Ubangiji ya ce a kan Yahowahaz, ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, wanda ya gāji sarautar ubansa, Yosiya, wanda ya tafi ya bar wurin nan. Ba zai ƙara komowa nan ba.
12. Amma a wurin da suka kai shi zaman talala, a can zai mutu, ba zai ƙara ganin wannan ƙasa ba.
13. Kaiton wanda ya gina gidansa tahanyar rashin adalci,Benayensa kuma ta hanyar rashingaskiya.Wanda ya sa maƙwabcinsa ya yimasa aiki a banza,Bai ba shi hakkinsa ba.
14. Kaiton wanda ya ce,“Zan gina wa kaina babban gidaDa waɗansu irin benayemusamman.”Ya yi masa tagogi,Ya manna masa itacen al'ul,Sa'an nan ya yi masa jan shafe.
15. Kana tsammani kai sarki ne,Da yake ƙasarka ta itacen al'ulce?Amma ubanka ya ci, ya sha,Ya yi gaskiya, ya aikata adalci,Ya kuwa zauna lafiya.
16. Ya biya wa matalauta da masubukata hakkinsu,Ya kuwa yi kyau.Abin da ake nufi da sanina ke nan,In ji Ubangiji.
17. Amma ka sa idonka da zuciyarka gaƙazamar riba,Da zubar da jinin marar laifi,Da yin zalunci da danniya.
18. Domin haka ga abin da Ubangiji ya ce a kan Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza,“Ba za su yi makoki dominsa ba, kosu ce,‘Wayyo ɗan'uwanmu!’ ko, ‘Wayyo'yar'uwarmu!’Ba za su yi makoki dominsa ba, suce,‘Wayyo ubangidanmu!’ ko ‘Wayyo mai martaba!’
19. Za a binne shi kamar jaki,Za a ja shi a yar a bayan ƙofofinUrushalima.”
20. Ku haura zuwa Lebanon, ku yikuka,Ku ta da muryarku cikin Bashan,Ku yi kuka daga Abarim,Gama an hallakar da dukanƙaunatattunku.
21. Ubangiji ya yi muku magana alokacin wadatarku.Amma kun ce, “Ba za mu kasakunne ba!”Wannan shi ne halinku tun kunasamari,Don ba ku yi biyayya da muryaUbangiji ba.