21. Yana da ikon sāke lokatai,Yakan tuɓe sarakuna, ya kuma naɗa waɗansu.Yana ba masu hikima hikima, masu ilimi kuwa fahimi,
22. Yana bayyana zurfafan abubuwa masu wuyar ganewa,Ya san abin da yake cikin duhu.Haske kuma yana zaune tare da shi.
23. A gare ka nake ba da godiya da yabo, ya Allah na kakannina,Gama ka ba ni hikima da iko,Har ka sanar mini da abin da muka roƙe ka,Ka sanar mana da matsalar da ta dami sarki.”
24. Sa'an nan Daniyel ya tafi wurin Ariyok wanda sarki ya sa ya karkashe masu hikima na Babila, ya ce masa, “Kada ka karkashe masu hikima na Babila, ka kai ni gaban sarki, ni kuwa zan yi wa sarki fassarar.”
25. Nan da nan kuwa Ariyok ya kai Daniyel gaban sarki, ya ce masa, “Na sami wani daga cikin kamammun ƙasar Yahuza wanda zai iya sanar wa sarki da fassarar.”
26. Sarki kuwa ya ce wa Daniyel, mai suna Belteshazzar, “Ka iya faɗa mini mafarkin duk da fassararsa?”
27. Daniyel ya amsa wa sarki, ya ce, “Ba masu hikima, ko masu dabo, ko masu sihiri, ko masu duba, da za su iya su warware wa sarki wannan matsala da ta dame shi.
28. Amma akwai Allah a Sama mai bayyana asirai, shi ne ya sanar wa sarki Nebukadnezzar da abin da zai faru a kwanaki masu zuwa. Mafarkinka da wahayinka waɗanda suka zo cikin tunaninka, sa'ad da kake kwance bisa gadonka ke nan.
29. “Ya maigirma, sa'ad da kake kwance a gadonka sai tunanin abin da zai faru nan gaba ya zo maka. Shi kuma wanda yake bayyana asirai ya sanar da kai abin da zai faru nan gaba.
30. Amma ba a bayyana mini wannan asiri saboda ina da wata hikima fiye da sauran mutane ba, sai dai domin a sanar wa sarki da fassarar, ka kuma san tunanin da ya shiga zuciyarka.
31. “Ya sarki, ka ga wani babban mutum-mutum mai walƙiya, mai bantsoro, yana tsaye a gabanka.
32. An yi kan mutum-mutumin da zinariya tsantsa. Ƙirji da damutsa, an yi su da azurfa, cikinsa da cinyoyinsa, an yi su da tagulla.
33. Da baƙin ƙarfe aka yi sharaɓansa, an yi ƙafafunsa da baƙin ƙarfe gauraye da yumɓu.
34. Sa'ad da kake cikin dubawa, sai aka gutsuro wani dutse ba da hannun mutum ba, aka bugi ƙafafunsa na baƙin ƙarfe gauraye da yumɓu, aka ragargaza shi.
35. Sa'an nan baƙin ƙarfen, da yumɓun, da tagullar, da azurfar, da zinariyar suka ragargaje gaba ɗaya, duka suka zama kamar ƙaiƙayi na masussuka da kaka. Iska kuwa ta kwashe su ta tafi da su, har ba a iya ganin ko alamarsu. Amma wannan dutse da ya buge mutum-mutumin ya girke, ya zama babban dutse ya cika duniya duka.