4. “Ku kasa kunne gare ni, ku mutanena,Ku saurara ga abin da nake faɗa,Na ba da koyarwata ga al'ummai,Dokokina za su kawo musu haske.
5. Zan zo da sauri in cece su,Lokacina na nasara ya yi kusa.Ni kaina zan yi mulki a kan al'ummai.Manisantan ƙasashe za su jira ni in zo,Za su jira da sa zuciya, ni in cece su.
6. Ku duba sammai, ku duba duniya!Sammai za su shuɗe kamar hayaƙi,Duniya kuwa za ta yage kamar tsohuwar tufa,Dukan mutanenta kuma za su mutu.Amma ceton da zan kawo zai dawwama har abada,Nasarata, ita ce za ta zama ta har abada.
7. “Ku kasa kunne gare ni, ku da kuka san abin da yake daidai,Ku da kuke riƙe da koyarwata a zuciyarku.Kada ku ji tsoro sa'ad da mutane suke yi muku ba'a da zagi.
8. Irin waɗannan mutane za su shuɗe kamar tufar da asu ya cinye!Amma ceton da zan kawo zai dawwama har abada,Nasarata za ta kasance har abada abadin.”
9. Ya Ubangiji, ka tashi, ka taimake mu!Ka nuna ikonka, ka cece mu,Ka nuna ikonka kamar yadda ka yi a dā.Kai ne ka daddatse dodon ruwa, wato Rahab.
10. Kai ne ka sa teku ta ƙafe,Ka kuma shirya hanya ta ruwa,Domin waɗanda kake cetonsu su haye.
11. Su waɗanda ka fansaZa su kai Urushalima da farin ciki,Da waƙa, da sowa ta murna.Za su yi ta murna har abada,Ba sauran baƙin ciki ko ɓacin zuciya har abada.
12. Ubangiji ya ce,“Ni ne wanda yake ƙarfafa ku.Don me za ku ji tsoron mutum mai mutuwa,Wanda bai fi ciyawa tsawon rai ba?
13. Kuna mantawa da Ubangiji wanda ya halicce ku,Wanda ya shimfiɗa sammai,Ya kuma kafa harsashin ginin duniya?Don me za ku yi ta jin tsoron fushin waɗanda suke zaluntarku,Da waɗanda suke shiri su hallaka ku?Fushinsu ba zai taɓa yi muku kome ba!
14. 'Yan sarƙa za su fita ba da jimawa baZa su yi tsawon rai,Su kuma sami dukan abincin da suke bukata.
15. “Ni ne Ubangiji Allahnku,Na dama tekuNa sa raƙumanta suka yi ruri.Sunana Ubangiji Mai Iko Dukka!