Irm 51:1-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ubangiji ya ce,“Ga shi, zan kawo iskar ɓarna akan BabilaDa mazaunan Kaldiya.

2. Zan aika da masu casawa zuwaBabila, za su casa ta,Su bar ƙasarta kango.Za su kewaye ta a kowane sashiA wannan ranar masifa.

3. Kada ku bar maharbi ya yi harbi dabakansa,Kada kuma ya sa kayan yaƙinsa,Kada ku rage samarinta,Ku hallaka dukan sojojinta.

4. Za su fāɗi matattu a ƙasarKaldiyawa,Za a sassoke su a titunansu.”

5. Allah na Isra'ila da Yahuza,Ubangiji Mai Runduna, bai yashesu ba,Ko da yake sun yi wa Mai Tsarki naIsra'ila zunubi.

6. Ku gudu daga cikin Babila,Bari kowa ya ceci ransa,Kada a hallaka ku tare da ita,Gama a wannan lokaci Ubangiji zaisāka mata,Zai sāka mata bisa ga alhakinta.

7. Babila ta zama ƙoƙon zinariya ahannun Ubangiji,Ta sa dukan duniya ta yi maye.Ƙasashen duniya sun sha ruwaninabinta, suka haukace.

8. Farat ɗaya, Babila ta fāɗi, takakkarye,Ku yi kuka dominta!Ku samo mata magani domin azabarda take sha, watakila ta warke.

9. Mun ba Babila magani, amma ba tawarke ba.Bari mu ƙyale ta, kowannenmu yakoma garinsu,Gama hukuncinta ya kai sammai, yayi tsawo har samaniya.

10. Ubangiji ya baratar da mu a fili,Bari mu tafi mu yi shelar aikinUbangiji Allahnmu a cikinSihiyona.

11. Ku wasa kibau, ku cikakwaruruwanku!Ubangiji ya ta da ruhun sarakunanMediyawa,Domin yana niyyar hallaka Babila.Gama Ubangiji zai yi ramuwasaboda Haikalinsa.

12. Ku ta da tuta don a faɗa wa garunBabila,Ku ƙarfafa matsara,Ku sa su su yi tsaro,Ku kuma sa 'yan kwanto!Ga shi, Ubangiji ya yi niyya, ya kuwaaikataAbin da ya faɗa a kan mazaunanBabila.

13. Ƙarshenki ya zo,Ke mai zama kusa da ruwa mai yawa,Mai yawan dukiya.Ajalinki ya auka.

14. Ubangiji Mai Runduna ya rantse dazatinsa, ya ce,“Hakika zan cika Babila da mutanekamar fāra,Za su kuwa raira waƙar nasara akanta.”

15. Ubangiji ne ya halicci ƙasa daikonsa,Ya kafa duniya da hikimarsa,Ya kuma shimfiɗa sammai dafahiminsa.

16. Bisa ga umarninsa ruwan da yakesamaniya yakan yi ruri,Yakan sa gajimare su tashi dagaƙarshen duniya,Yakan sa walƙiya ta walƙata cikinruwan sama,Yakan sa iska ta haura daga cikintaskokinsa.

17. Kowane ɗan adam wawa ne, mararilimi,Kowane maƙerin zinariya kuma zaisha kunya daga wurin gumakansa,Gama siffofinsa na ƙarya ne, banumfashi a cikinsu.

Irm 51