18. Ta ɗauka, ta koma gari, ta nuna wa surukarta abin da ta kalato. Ta kuma kawo mata sauran abincin da ta ci ta ƙoshi har ta rage.
19. Surukarta kuma ta ce mata, “A ina kika yi kala yau? A gonar wa kika yi aiki? Albarka ta tabbata ga wannan mutum wanda ya kula da ke.”Sai ta faɗa mata sunan mutumin da ta yi kala a gonarsa, ta ce, “Sunan mutumin da na yi kala a gonarsa yau, Bo'aza.”
20. Na'omi ta ce wa Rut, “Ubangiji wanda bai daina nuna alheri ga masu rai da marigayan ba, ya sa masa albarka.” Ta ƙara da cewa, “Ai, mutumin, shi danginmu ne na kusa.”
21. Rut kuma, mutuniyar Mowab, ta ce, “Banda wannan ma, ya ce mini, ‘Ki riƙa bin barorina, har lokacin da suka gama mini girbin.’ ”
22. Sa'an nan Na'omi ta ce wa Rut, “Madalla, 'yata, ki riƙa bin 'yan matan gidansa, kada ki tafi wata gona dabam.”
23. Sai ta riƙa bin 'yan matan gidan Bo'aza. Ta yi ta kala har aka gama girbin sha'ir da na alkama, tana zaune tare da surukarta, wato Na'omi.