11. Ka yi hanya ta cikin teku domin jama'arka,Ka sa su bi ta ciki a kan sandararriyar ƙasa.Ka sa waɗanda suke fafararsu suka hallaka cikin zurfin teku,Suka nutse kamar dutse.
12. Da rana ka bishe su da al'amudin girgije,Da dare ka bishe su da al'amudin wuta.
13. Ka kuma sauka a bisa Dutsen Sinai,Ka yi magana da jama'arka a can,Ka ba su ka'idodin da suka dace,Da dokoki, da kyakkyawar koyarwa.
14. Ka koya musu su kiyaye Asabar ɗinka tsattsarka,Ka kuma ba su dokokinka ta hannun Musa bawanka.
15. Ka ba su abinci daga sama sa'ad da suka ji yunwa,Ruwa kuma daga dutse sa'ad da suka ji ƙishi,Ka faɗa musu su shiga su mallaki ƙasar da ka yi alkawari za ka ba su.
16. Amma kakanninmu suka yi fāriya, suka taurare,Suka ƙi yin biyayya da umarnanka.
17. Suka ƙi yin biyayya,Suka manta da dukan abin da ka yi,Suka manta da al'ajaban da ka aikata.Cikin fāriyarsu suka zaɓi shugaba,Don su koma cikin bauta a Masar.Amma kai Allah ne mai gafartawa,Kai mai alheri ne, mai ƙauna,Jinƙanka da girma yake, ba ka yashe su ba.
18. Ko sa'ad da suka yi wa kansu ɗan marakin zubi,Suka ce shi ne allahn da ya fisshe su daga Masar,Ai, sun yi maka ɓatanci, ya Ubangiji.
19. Amma ba ka rabu da su a hamada ba,Saboda jinƙanka mai girma ne.Ba ka kuwa kawar da girgije da wuta ba,Waɗanda suke nuna musu hanya dare da rana.
20. Ta wurin alherinka ka faɗa musu abin da ya kamata su yi,Ka ciyar da su da manna, ka ba su ruwa su sha.
21. Ka taimake su a jeji shekara arba'in,Ka ba su dukan abin da suke bukata,Ƙafafunsu ba su kumbura su yi musu ciwo ba.
22. “Ka sa sun ci al'ummai da mulkoki da yaƙi,Ƙasashen da suke maƙwabtaka da tasu.Suka ci ƙasar Sihon, Sarkin Heshbon,Da ƙasar Bashan, inda Og yake sarki.
23. Ka riɓaɓɓanya zuriyarsu kamar taurarin sararin sama,Ka sa suka ci ƙasar, suka zauna cikinta,Ƙasar da aka yi wa kakanninsu alkawari za ka ba su.
24. Saboda haka zuriyarsu suka shiga, suka mallaki ƙasar Kan'ana.Ka rinjayi mutanen da suke zama a can.Ka ba jama'arka iko su yi yadda suke soDa mutane, da sarakunan ƙasar Kan'ana.
25. Sun ci birane masu garu, da ƙasa mai dausayi,Da gidaje cike da dukiya, da rijiyoyi, da gonakin inabi,Da itatuwan zaitun, da itatuwa masu 'ya'ya.Suka ci dukan abin da suke so, suka yi taiɓa,Suka mori dukan kyawawan abubuwan da ka ba su.
26. “Amma suka yi maka rashin biyayya, suka tayar maka,Suka juya wa dokokinka baya,Suka karkashe anna bawan da suka faɗakar da su,Waɗanda suka faɗa musu su juyo gare ka.Suka yi ta saɓa maka lokaci lokaci.
27. Saboda haka ka bar abokan gābansu su ci su, mallake su.A wahalarsu sun yi kira gare ka domin taimako,Ka kuwa amsa musu daga Sama.Ta wurin jinƙanka mai yawa ka aiko musu da shugabanni,Waɗanda suka kuɓutar da su daga maƙiyansu.