Josh 15:17-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Otniyel kuwa, ɗan Kenaz, ɗan'uwan Kalibu, ya ci Kiriyat-sefer. Kalibu kuwa ya ba shi Aksa 'yarsa aure.

18. Da ta zo wurinsa, ya zuga ta ta roƙi mahaifinta saura. Da ta sauka daga kan jakinta, sai Kalibu ya ce mata, “Me kike so?”

19. Ta kuwa ce masa, “Ka yi mini alheri, da yake ka tura ni a ƙasar Negeb, ina roƙonka ka ba ni maɓuɓɓugar ruwa.” Kalibu kuwa ya ba ta maɓuɓɓugar tuddai da na kwari.

20. Wannan shi ne gādon jama'ar Yahuza bisa ga iyalansu.

21. Biranen jama'ar Yahuza da suke can kudu sosai wajen iyakar Edom, su ne Kabzeyel, da Eder, da Yagur,

22. da Kina, da Dimona, da Adada,

23. da Kedesh, da Hazor, da Yitnan,

24. da Zif, da Telem, da Beyalot,

25. da Hazor-hadatta, da Kiriyot-hesruna, wato Hazor,

Josh 15