Ish 49:6-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Ubangiji ya ce mini,“Bawana, ina da aiki mai girma dominka,Ba komo da girman jama'ar Isra'ila da suka ragu kaɗai ba,Amma zan sa ka zama haske ga al'ummai,Domin dukan duniya ta tsira.”

7. Allah Mai Tsarki na Isra'ila, Mai Fansa,Ya ce wa wanda aka raina ƙwarai,Al'ummai suka ƙi shi,Bawa na masu mulki kuma,“Sarakuna za su gan ka a sake,Su kuma miƙe tsaye su ba ka girma,Shugabanni su kuma za su gani,Su rusuna har ƙasa su ba ka girma.”Wannan kuwa zai faru saboda Ubangiji,Allah Mai Tsarki na Isra'ila, ya zaɓi bawansa,Ya kuwa cika alkawaransa.

8. Ubangiji ya ce wa jama'arsa,“Idan lokacin da zan cece ku ya yi, zan nuna muku alheri.Zan ji kukanku in taimake ku.Zan tsare ku in kiyaye ku,Zan kuwa yi wa dukan mutane alkawari ta wurinku.Zan bar ku ku sāke zama a ƙasarku wadda take kufai a yanzu.

9. Zan ce wa 'yan kurkuku, ‘Ku tafi na sake ku!’Waɗanda suke cikin duhu kuwa, in ce musu,‘Ku fito zuwa wurin haske!’Za su zama kamar tumakin da suke kiwo a tuddai,

10. Ba za su taɓa jin yunwa ko ƙishi ba.Ba za su sha zafin rana da na hamada ba,Gama wanda yake ƙaunarsu ne zai bi da su.Zai bi da su zuwa maɓuɓɓugan ruwa.

11. “Zan yi babbar hanya ta kan duwatsu,In kuma shirya hanya domin mutanena su bi.

12. Mutanena za su zo daga can nesa,Daga Birnin Sin a kudu,Daga yamma, da arewa.”

13. Ku raira, ku sammai! Ki yi sowar murna, ke duniya!Bari duwatsu su ɓarke da waƙa!Ubangiji zai ta'azantar da mutanensa,Zai ji juyayin mutanensa da suke shan wahala.

14. Amma mutanen Urushalima suka ce,“Ubangiji ya yashe mu!Ya manta da mu.”

15. Saboda haka Ubangiji ya amsa ya ce,“Mace za ta iya mantawa da jaririnta,Ta kuma ƙi ƙaunar ɗan da ta haifa?Ya yiwu mace ta manta da ɗanta,To, ni ba zan taɓa mantawa da ku ba.

Ish 49