12. Na faɗi abin da zai faruSa'an nan na zo domin taimakonku.Ba wani gunkin da ya taɓa yin haka,Ku ne shaiduna.
13. Ni ne Allah, haka kuwa nake tutur,Ba wanda zai iya tserewa daga ikona,Ba mai iya sāke abin da na riga na yi.”
14. Allah Mai Tsarki na Isra'ila, Ubangiji wanda ya fanshe ku ya ce,“Domin in cece ku zan aiko sojoji gāba da Babila,Zan rushe ƙofofin birni,Sowar mutanen birnin za ta zama kuka.
15. Ni ne Ubangiji, Allahnku Mai Tsarki na Isra'ila,Ni na halicce ku, ni ne kuma sarkinku.”
16. Tuntuni Ubangiji ya shirya hanya ta cikin teku,Da turba kuma a cikin ruwa.
17. Ya bi da manyan sojoji zuwa hallaka,Sojojin karusai da na dawakai.Sun faɗi warwar, ba za su ƙara tashi ba,An hure su kamar 'yar wutar fitila!
18. Amma Ubangiji ya ce,“Kada ku maƙale wa abubuwan da suka wuce,Ko ku riƙa tunanin abin da ya faru tuntuni.
19. Ku duba abin da nake shirin yi.Yana ta faruwa ma, kuna iya ganinsa yanzu!Zan yi hanya a cikin jeji,In kuma ba ku rafuffukan ruwa a can.
20. Har da namomin jeji za su girmama ni,Diloli da jiminai za su yi yabonaSa'ad da na sa kogunan ruwa su yi gudu a hamada,Domin su ba da ruwa ga zaɓaɓɓun mutanena.
21. Su ne mutanen da na yi domin kaina,Za su raira yabbaina!”
22. Ubangiji ya ce,“Amma ba ni kuka yi wa sujada ba,Kun gaji da ni, ya Isra'ila.
23. Ba ku kawo mini hadayun ƙonawa na tumaki ba,Ba ni kuke girmamawa da hadayunku ba.Ban nawaita muku da neman hadayu ba,Ko in gajiyar da ku da roƙon turare.
24. Ba ku sayi turare domina ba,Ko ku gamshe ni da kitsen dabbobinku.Maimakon haka, sai kuka nawaita mini da zunubanku,Kuka gajiyar da ni da abubuwan da kuke aikatawa da ba daidai ba.
25. Duk da haka, ni ne Allah wanda ya shafe zunubanku,Na kuwa yi haka saboda yadda nake.Ba zan ƙara tunawa da zunubanku kuma ba.