43. Garuruwanta sun zama abinƙyama,Ta zama hamada, inda ba ruwa,Ƙasar da ba mazauna,Ba kuma mutumin da zai ratsa tacikinta.
44. Zan hukunta Bel, gunkin Babila,Zan sa ya yi aman abin da yahaɗiye,Ƙasashen duniya ba za su ƙarabumbuntowa wurinsa ba.Garun Babila ya rushe!”
45. “Ku fito daga cikinta, ya jama'ata,Kowa ya tsere da ransa daga zafinfushin Ubangiji.
46. Kada zuciyarku ta yi suwu,Kada kuma ku ji tsoro sabodalabarin da ake ji a ƙasar,Labari na wannan shekara dabam,na wancan kuma dabam,A kan hargitsin da yake a ƙasar,Mai mulki ya tasar wa mai mulki.
47. Saboda haka kwanaki suna zuwa,Sa'ad da zan hukunta gumakanBabila,Za a kunyatar da dukan ƙasarBabila,Dukan matattunta za su faɗi atsakiyarta.
48. Sa'an nan sama da duniya, da dukanabin da take cikinsu,Za su raira waƙar farin ciki,Domin masu hallakarwa daga arewada za su auko mata,Ni Ubangiji na faɗa.”
49. Babila za ta fāɗi,Saboda mutanen Isra'ila da dukanmutanen duniya waɗanda takashe.
50. Ku waɗanda kuka tsere wa takobi!Ku gudu! Kada ku tsaya!Ku tuna da Ubangiji a can nesa indakuke,Ku kuma yi ta tunawa daUrushalima.
51. Mun sha kunya saboda zargin da akeyi mana,Kunya ta rufe mu,Gama baƙi sun shiga tsarkakanwurare na Haikalin Ubangiji.
52. “Domin haka kwanaki suna zuwa,”in ji Ubangiji,“Sa'ad da zan hukunta gumakanBabila, da dukan ƙasarta,Waɗanda aka yi wa rauni, za su yinishi.
53. Ko da Babila za ta hau samaniya,Ta gina kagara mai ƙarfi a can,Duk da haka zan aiki masuhallakarwa a kanta,Ni Ubangiji na faɗa.”
54. Ku ji muryar kuka daga Babila,Da hargowar babbar hallakarwadaga ƙasar Kaldiyawa!
55. Gama Ubangiji yana lalatar daBabila,Yana kuma sa ta kame bakinta naalfarma,Sojoji suna kutsawa kamar raƙumanruwa,Suna ta da muryoyinsu.
56. Gama mai hallakarwa ya auka waBabila,An kama sojojinta,An kuma kakkarya bakunansu,Gama Ubangiji shi Allah ne, maisakayya,Zai yi sakayya sosai.
57. “Zan sa mahukuntanta, da masuhikimarta,Da masu mulkinta, dashugabanninta,Da sojojinta su sha su yi maye.Za su dinga yin barcin da ba za sufarka ba,”In ji Sarkin, mai suna Ubangiji MaiRunduna.
58. “Ni Ubangiji Mai Runduna, na ce,Za a baje garun nan na Babila maifāɗiZa a kuma ƙone dogayenƙyamarenta da wuta.Mutane sun wahalar da kansu abanza.Sauran al'umma sun yi wahala kawaidomin wutar lalata.”
59. Jawabin da annabi Irmiya ya ba Seraiya, ɗan Neriya, wato jikan Ma'aseya, lokacin da ya tafi tare da Zadakiya, Sarkin Yahuza, zuwa Babila a shekara ta huɗu ta mulkinsa. Seraiya shi ne shugaba mai lura da gidajen saukar baƙi.