33. Ni Ubangiji Mai Runduna, Allah naIsra'ila na ce,“Mutanen Babila sun zama kamardaɓen masussukaA lokacin da ake sussuka,Ba kuwa da daɗewa ba lokacin girbeta zai zo.”
34. Nebukadnezzar, Sarkin Babila, yacinye Urushalima,Ya ragargaza ta,Ya maishe ta kufai,Ya haɗiye ta kamar yadda dodonruwa yakan yi,Ya cika cikinsa da kayanmarmarinta,Ya tatse ta sarai.
35. Bari mutanen Sihiyona su ce,“Allah ya sa muguntar da mutanenBabila suka yi mana ta komakansu!”Bari kuma mutanen Urushalima suce,“Allah ya sa hakkin jininmu ya komakan Kaldiyawa!”
36. Ubangiji ya ce,“Zan tsaya muku,Zan ɗaukar muku fansa,Zan sa tekunsu da maɓuɓɓugarsu suƙafe.
37. Babila za ta zama tarin juji, wurinzaman diloli,Abar ƙyama da abar ba'a, inda bakowa.
38. Mutanen Babila za su yi ruri kamarzakuna,Su yi gurnani kamar 'ya'yan zaki.
39. Sa'ad da suke cike da haɗama zan yimusu biki,In sa su sha, su yi maye, su yimurna.Za su shiga barcin da ba za su farkaba.
40. Zan kai su mayanka kamar 'yanraguna, da raguna, da bunsurai.
41. “An ci Babila,Ita wadda duniya duka take yabo ancinye ta da yaƙi,Ta zama abar ƙyama ga sauranal'umma!
42. Teku ta malalo a kan Babila,Raƙuman ruwa masu hauka sunrufe ta.
43. Garuruwanta sun zama abinƙyama,Ta zama hamada, inda ba ruwa,Ƙasar da ba mazauna,Ba kuma mutumin da zai ratsa tacikinta.