18. Abin da zai faru ga Edom zai zama daidai da abin da ya faru ga Saduma, da Gwamrata, da biranen da suke kusa da su, a lokacin da aka kaɓantar da su. Ba wanda zai zauna cikinta, ba wanda kuma zai yi zaman baƙunci a cikinta, ni Ubangiji na faɗa.
19. Kamar yadda zaki yakan fito daga cikin kurmin Urdun, garin ya fāda wa babban garken tumaki, haka zan sa nan da nan su gudu daga gare ta. Zan naɗa wani wanda na zaɓa, gama wa yake kama da ni? Wa zai yi ƙarata? Ina makiyayin da ya isa ya yi gāba da ni?
20. Domin haka, ku ji shirin da ni Ubangiji na yi wa Edom, da abin da nake nufin yi wa mazaunan Teman. Hakika za a tafi da su, har da ƙanana na garken tumaki, zan kuma sa wurin kiwonsu ya zama ƙeƙuwa saboda su.
21. Amon fāɗuwarsu zai sa ƙasa ta girgiza, za a kuma ji muryar kukansu har a Bahar Maliya.
22. Wani zai tashi da sauri, ya yi sama kamar gaggafa. Zai buɗe fikafikansa a kan Bozara. Zukatan sojojin Edom za su zama kamar zuciyar macen da take naƙuda.”
23. Ga abin da Ubangiji ya faɗa a kan Dimashƙu,“Hamat da Arfad sun gigice,Domin sun ji mugun labari,sun narke saboda yawan damuwa,Ba za su iya natsuwa ba.
24. Dimashƙu ta yi halin ƙaƙa naka yi,Ta juya, ta gudu,Tsoro ya kama ta,Azaba da baƙin ciki sun kama takamar na naƙuda.
25. Ƙaƙa aka manta da sanannen birni,Birnin da take cike da murna?
26. A waccan rana samarinta za su fāɗi adandalinta.Za a hallaka sojojinta duka,Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.
27. Zan kuma sa wuta a garun Dimashƙu,Za ta kuwa cinye fādodinBen-hadad.”
28. Ga abin da Ubangiji ya faɗa a kan Kedar da sarakunan Hazor, waɗanda sarki Nebukadnezzar ya ci da yaƙi,“Ku tashi zuwa Kedar,Ku hallaka mutanen gabas.
29. Za a kwashe alfarwansu dagarkunansu,Da labulan alfarwansu, da dukankayansu.Za a kuma tafi da raƙumansu,Za a gaya musu cewa, ‘Razana takewaye ku!’
30. “Ku mazaunan Hazor, ku gudu zuwanesa,Ku ɓuya cikin zurfafa, ni Ubangiji nafaɗa,Gama Nebukadnezzar, SarkinBabila, ya shirya mukumaƙarƙashiya,Ya ƙulla mugun nufi game da ku.
31. Ku tashi ku fāɗa wa al'ummar da takezama lami lafiya,Waɗanda ba su da ƙofofi ko ƙyamare,Suna zama su kaɗai.
32. “Za a washe raƙumansu dagarkunan shanunsu ganima,Zan watsar da masu yin kwaskwasko'ina,Zan kuma kawo musu masifu dagakowace fuska,Ni Ubangiji na faɗa.
33. Hazor za ta zama kufai har abada,wurin zaman diloli,Ba wanda zai zauna a ciki, ba wandakuma zai yi zaman baƙunci a wurin.”
34. Maganar da Ubangiji ya yi wa annabi Irmiya a kan Elam a farkon sarautar Zadakiya Sarkin Yahuza.
35. Ubangiji Mai Runduna ya ce,“Zan karya bakan Elam, indaƙarfinta yake.
36. Zan sa iska ta hura a kan Elam dagakusurwoyi huɗu na samaniya.Za ta watsar da mutane ko'ina,Har ba ƙasar da za a rasa mutuminElam a ciki.
37. Zan sa mutanen Elam su ji tsoronmaƙiyansu waɗanda suke nemanransu.Da zafin fushina zan kawo musumasifa,In sa a runtume su da takobi,Har in ƙare su duka,Ni Ubangiji na faɗa.
38. Zan kafa gadon sarautata a Elam,Zan hallaka sarkinta dashugabanninta.