1. Ubangiji ya ce, “Lokaci yana zuwa da zan zama Allah na dukan iyalan Isra'ila, za su kuwa zama jama'ata.”
2. Haka Ubangiji ya ce, “Jama'ar dasuka tsere wa takobi,Sun sami alheri a cikin jeji,A sa'ad da Isra'ila suka nemihutawa.”
5. Za ki sāke dasa gonar inabiA kan duwatsun Samariya,Masu dashe za su dasa,Za su mori 'ya'yan.
6. Gama rana tana zuwa sa'ad da maitsaro zai yi kiraA ƙasar tudu ta Ifraimu, ya ce,‘Ku tashi mu haura zuwa SihiyonaZuwa wurin Ubangiji Allahnmu.’ ”
7. Ga abin da Ubangiji ya ce,“Raira wa Yakubu waƙar farin cikida ƙarfi,Ku ta da murya saboda shugabanal'ummai,Ku yi shela, ku yi yabo, ku ce,‘Ya Ubangiji ka ceci jama'arka,Wato ringin mutanen Isra'ila,’
8. Ga shi, zan fito da su daga ƙasararewa,Zan tattaro su daga manisantanwurare na duniya,Tare da su makafi da guragu,Da mace mai goyo da mai naƙuda,Za su komo nan a babbar ƙungiya.
9. Da kuka za su komo.Da ta'aziyya zan bishe su, in komarda su,Zan sa su yi tafiya a gefen rafuffukanruwa,A kan miƙaƙƙiyar hanya, inda baza su yi tuntuɓe ba.Gama ni uba ne ga Isra'ila,Ifraimu kuwa ɗan farina ne.”
10. “Ku ji maganar Ubangiji,Ya ku al'ummai,Ku yi shelarsa har a ƙasashen da sukenesa, na gāɓar teku.Ku ce, ‘Shi wanda ya warwatsaIsra'ila zai tattaro ta,Zai kiyaye ta kamar yadda makiyayiyakan kiyaye garkensa.’
11. Gama Ubangiji ya fanshi Yakubu.Ya fanshe shi daga hannuwanwaɗanda suka fi ƙarfinsa.