1 Tar 21:13-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Dawuda kuwa ya ce wa Gad, “Na shiga uku, gara in fāɗa a hannun Ubangiji, gama shi mai yawan jinƙai ne, kada ka bar ni in faɗa a hannun mutum.”

14. Saboda haka Ubangiji ya aiko da annoba a kan Isra'ila. Mutum dubu saba'in (70,000) na Isra'ila suka mutu.

15. Allah ya aiko mala'ikansa don ya hallaka Urushalima, amma sa'ad da yake gab da hallaka ta, sai Ubangiji ya gani, ya janye shirin annobar, ya ce wa mala'ikan hallakarwa, “Ya isa, janye hannunka.” Mala'ikan Ubangiji kuwa na tsaye kusa da masussukar Arauna Bayebuse.

16. Dawuda ya ɗaga idonsa, sai ya ga mala'ikan Ubangiji yana tsakanin sama da ƙasa, da takobinsa a zare a hannunsa a kan Urushalima. Sa'an nan Dawuda tare da dattawa suka fāɗi rubda ciki, suna saye da tufafin makoki.

17. Dawuda ya ce wa Allah, “Ai, ni ne na ba da umarni a ƙidaya jama'ar. Hakika, ni na yi zunubi, na kuwa aikata mummunan abu, amma waɗannan talakawa fa, me suka yi? Ya Ubangiji Allahna, ka bar hannunka ya yi gāba da ni da gidan tsohona, amma kada ka yi gāba da jama'arka, har da za ka aukar musu da annoba.”

18. Mala'ikan Ubangiji ya umarci Gad ya faɗa wa Dawuda ya haura, ya gina wa Ubangiji bagade a masussukar Arauna Bayebuse.

19. Dawuda kuwa ya haura kamar yadda Gad ya faɗa masa da sunan Ubangiji.

20. Arauna yana cikin sussukar alkama, sai ya waiwaya ya ga mala'ika. 'Ya'yansa maza su huɗu kuwa, waɗanda suke tare da shi suka ɓuya.

21. Sa'ad da Dawuda ya tafi wurin Arauna, da Arauna ya ga Dawuda, sai ya fito daga masussukar ya tafi ya fāɗi rub da ciki a gaban Dawuda ya gaishe shi.

22. Sai Dawuda ya ce masa, “Ka ba ni wannan masussuka don in gina wa Ubangiji bagade. Ka sayar mini da masussukar a bakin cikakken kuɗinta, domin a kawar wa jama'a da annobar.”

1 Tar 21