1. Ku busa ƙaho, ku yi gangami,A cikin Sihiyona, tsattsarkandutsen Allah!Duk mutanen ƙasar za su yi rawarjiki,Domin ranar Ubangiji tana zuwa, tayi kusa.
2. Za ta zama rana ce mai duhudulum,Ranar gizagizai ce baƙi ƙirin.Runduna mai ƙarfi tana tasowa,Kamar ketowar hasken safiya bisatsaunuka.Faufau ba a taɓa ganin irinta ba,Ba kuwa za a sāke ganin irinta ba.
3. Tana cinye shuke-shuke kamar wuta,Ƙasa kamar gonar Adnin take kafinta zo,Amma a bayanta ta zama hamada,Ba abin da ya tsere mata.
4. Kamar doki take,Tana gudu kamar dokin yaƙi.
5. Motsin tsallenta a kan duwatsukamar Motsin karusa ne.Kamar kuma amon wutar da take cintattaka.Kamar runduna mai ƙarfi wadda taja dāgar yaƙi.
6. Da zuwanta mutane sukan firgita,Dukan fuskoki sukan ɓaci.
7. Takan auka kamar mayaƙa,Takan hau garu kamar sojoji,Takan yi tafiya,Kowa ta miƙe sosai inda ta sagaba,Ba ta kaucewa.