4. Amma Yahuza Iskariyoti, ɗaya daga cikin almajiransa, wato wanda zai bāshe shi, ya ce,
5. “Me ya hana a sayar da man nan a kan dinari ɗari uku, a ba talakawa kuɗin?”
6. Ya faɗi haka fa, ba wai don yana kula da gajiyayyu ba, a'a, sai dai don shi ɓarawo ne, da yake kuma jakar kuɗinsu tana hannunsa, yakan riƙa taɓa abin da yake ciki.
7. Sai Yesu ya ce, “A ƙyale ta, dā ma ta ajiye shi domin tanadin ranar jana'izata.
8. Ai, kullum kuna tare da gajiyayyu, amma ba kullum kuke tare da ni ba.”
9. Da taron Yahudawa mai yawa suka ji labari yana nan, sai suka zo, ba domin Yesu kaɗai ba, har ma don su ga Li'azaru wanda ya tasa daga matattu.
10. Sai manyan firistoci suka yi shawarar kashe Li'azaru, shi ma,
11. domin ta dalilinsa Yahudawa da yawa suke warewa, suna gaskatawa da Yesu.
12. Kashegari babban taron da suka zo idi, da suka ji Yesu yana zuwa Urushalima,
13. suka ɗaɗɗauko gazarin dabino suka firfita taryensa, suna ta da murya suna cewa, “Hosanna! Albarka ta tabbata ga mai zuwa da sunan Ubangiji, Sarkin Isra'ila!”
14. Da Yesu ya sami wani jaki sai ya hau, yadda yake a rubuce cewa,