Rom 9:22-28 Littafi Mai Tsarki (HAU)

22. To, ƙaƙa fa? Allah da yake yana so ya nuna fushinsa, ya kuma bayyana ikonsa, sai ya haƙura matuƙar haƙuri da waɗanda suka cancanci fushinsa, suka kuma isa hallaka,

23. Nufinsa ne yă bayyana yalwar ɗaukakarsa ga waɗanda ya yi wa jinƙai, wato, waɗanda dā ma ya yi wa tanadin ɗaukaka?

24. Wato, mu ke nan da ya kira, ba kuwa daga cikin Yahudawa kaɗai ba, har ma daga cikin al'ummai.

25. Kamar dai yadda ya faɗa a Littafin Yusha'u cewa,“Waɗanda dā ba jama'ata ba,Zan ce da su ‘jama'ata,’Wadda dā ba abar ƙaunata ba kuma,Zan ce da ita ‘abar ƙaunata.’ ”

26. “A daidai wurin da aka ce da su, ‘Ku ba jama'ata ba ne,’A nan ne za a kira su ‘'ya'yan Allah Rayayye,’ ”

27. A game da Isra'ila Ishaya ma ya ɗaga murya ya ce, “Ko da yake yawan Isra'ilawa ya kai kamar yashin teku, duk da haka kaɗan ne za su sami ceto.

28. Domin Ubangiji zai zartar da hukuncinsa a duniya, ya gama shi tashi ɗaya.”

Rom 9