Mar 5:33-36 Littafi Mai Tsarki (HAU)

33. Matar kuwa da ta san abin da aka yi mata, sai ta zo a tsorace, tana rawar jiki, ta fāɗi a gabansa, ta faɗa masa ƙashin gaskiya.

34. Sai ya ce mata, “'Yata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya, ki warke daga cutarki.”

35. Yana cikin magana, sai ga waɗansu daga gidan shugaban majami'a suka ce, “Ai, 'yarka ta rasu, me kuma za ka wahalar da Malamin?”

36. Amma Yesu bai kula da abin da suka faɗa ba, ya ce wa shugaban majami'a, “kada ka ji tsoro, ka ba da gaskiya kawai.”

Mar 5