Ish 47:14-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

14. “Za su zama kamar budu,Wuta kuwa za ta ƙone su ƙurmus!Ba ma za su ko iya ceton kansu ba.Harshen wuta zai fi ƙarfinsu,Ba wutar da za su zauna, su ji ɗumi!

15. Nan ne inda shawararsu za ta kai ki,Waɗannan masanan taurari da kika yi ta neman shawararsu dukan kwanakin ranki.Dukansu za su bar ki, kowa ya tafi inda ya nufa,Ba wanda zai ragu da zai cece ki.”

Ish 47