6. “Mutanena sun zama kamar ɓatattuntumaki,Waɗanda makiyayansu suka bauɗarda su,Suka ɓata a cikin tsaunuka,Suna kai da kawowa daga wannandutse zuwa wancan.Sun manta da shingensu.
7. Duk waɗanda suka same su, suncinye su.Maƙiyansu suka ce, ‘Ba mu yi laifiba,’Gama sun yi wa Ubangiji laifi,wanda yake tushen gaskiya,Ubangiji wanda kakanninsu sukadogara gare shi.
8. “Ku gudu daga cikin Babila,Ku fita kuma daga cikin ƙasarKaldiyawa,Ku zama kamar bunsurai waɗandasuke ja gaban garke.
9. Ga shi, zan kuta manyan ƙasashedaga arewaSu faɗa wa Babila da yaƙi.Za su ja dāgar yaƙi gāba da ita, sucinye ta.Kibansu kamar na gwanayenmayaƙa neWaɗanda ba su komowa banza.
10. Za a washe Kaldiyawa,Waɗanda suka washe su kuwa za suƙoshi,Ni Ubangiji na faɗa.
11. “Saboda kuna murna, kuna farinciki,Ku da kuka washe gādona,Saboda kuma kuna tsalle kamarkarsana a cikin ciyawa,Kuna haniniya kamar ingarmu,
12. Domin haka za a kunyatar da Babilasosai, inda kuka fito.Za ta zama ta baya duka a cikinsauran al'umma,Za ta zama hamada, busasshiyarƙasa.
13. Saboda fushin Ubangiji, ba wandazai zauna a cikinta,Za ta zama kufai,Duk wanda ya bi ta wajen Babila, zaiji tsoro,Zai kuma yi tsaki sabodalalacewarta.
14. “Dukanku 'yan baka, ku ja dāga, kukewaye Babila,Ku harbe ta, kada ku rage kibanku,Gama ta yi wa Ubangiji zunubi.
15. Ku kewaye ta da kuwwar yaƙi!Ta ba da gari,Ginshiƙanta sun fāɗi.An rushe garunta,Gama wannan sakayya ce taUbangiji.Ku sāka mata, ku yi mata kamaryadda ta yi.
16. Ku datse wa Babila mai shuka,Da mai yanka da lauje a lokacingirbi.Saboda takobin azzalumi,Kowa zai koma wurin mutanensa,Kowa kuma zai gudu zuwaƙasarsa.”
17. “Isra'ilawa kamar tumaki ne waɗanda zakuna suka bi su suna kora. Da farko dai Sarkin Assuriya ne ya cinye su. Yanzu kuwa Sarkin Babila, wato Nebukadnezzar, shi ne yake gaigayi ƙasusuwansu.
18. Saboda haka ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila na ce, zan yi wa Sarkin Babila da ƙasarsa hukunci, kamar yadda na hukunta Sarkin Assuriya.
19. Zan komar da Isra'ila a makiyayarsa, zai yi kiwo a Karmel da Bashan. Zai sami biyan bukatarsa a tsaunukan Ifraimu da na Gileyad.