Irm 48:11-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

11. “Tun daga ƙuruciya Mowab tanazama lami lafiya,Hankali kwance,Ba a jujjuya ta daga tulu zuwa tuluba,Ba a taɓa kai ta bauta ba,Domin haka daɗin ɗanɗanonta bairabu da ita ba,Ƙanshinta kuma bai sāke ba.”

12. Ubangiji ya ce, “Domin haka kwanaki suna zuwa, sa'ad da zai aika da mutane su tuntsurar da tuluna, su zubar da ruwan inabi, su farfasa tulunanta.

13. Sa'an nan Kemosh zai kunyatar da Mowab, kamar yadda Betel wadda Isra'ilawa suka dogara gare ta ta kunyatar da su.

14. “Don me kake cewa,‘Mu jarumawa ne, mayaƙan gaske?’

15. Mai hallaka Mowab da garuruwantaya taho,Zaɓaɓɓun majiya ƙarfinta sungangara mayanka,Ni sarki, mai suna Ubangiji MaiRunduna, na faɗa.

Irm 48