Irm 36:1-3 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. A sa'ad da Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, yana shekara huɗu da sarauta, sai Ubangiji ya yi magana da Irmiya, ya ce,

2. “Ka ɗauki takarda, ka rubuta dukan maganar da na yi maka a kan Isra'ila, da Yahuza, da dukan al'ummai, tun daga ran da na fara yi maka magana a zamanin Yosiya har ya zuwa yau.

3. Mai yiwuwa ne idan mutanen Yahuza suka ji dukan masifar da na yi niyya in aukar musu da ita, za su bar mugayen ayyukansu don in gafarta musu muguntarsu da zunubinsu.”

Irm 36