Irm 35:17-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Domin haka, ni Ubangiji Allah Mai Runduna, Allah na Isra'ila, na ce zan kawo wa mutanen Yahuza da mazaunan Urushalima masifar da na ce zan kawo musu, domin na yi musu magana, ba su ji ba, na kira su, ba su amsa ba.”

18. Sai Irmiya ya ce wa Rekabawa, “Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila ya ce, ‘Tun da yake kun kiyaye dukan abin da Yonadab kakanku ya umarce ku,

19. saboda haka Yonadab ɗan Rekab ba zai taɓa rasa magaji wanda zai tsaya a gabana ba.’ ”

Irm 35