26. “Kamar yadda ɓarawo yakan shakunya sa'ad da aka kama shi,Haka nan mutanen Isra'ila za su shakunya,Da su, da sarakunansu, dashugabanninsu,Da firistocinsu, da annabawansu.
27. Waɗanda suka ce wa itace, ‘Kai nemahaifinmu.’Suna kuma ce wa dutse, ‘Kai, kahaife mu.’Gama sun ba ni baya, ba su fuskanceni ba.Amma sa'ad da suke shan wahala,sukan ce,‘Ka zo ka taimake mu.’
28. Ina gumakan da kuka yi wakanku?Bari su tashi in sun iya cetonkulokacin wahalarku.Yahuza, yawan gumakanku sun kaiYawan garuruwanku.
29. Ni Ubangiji, ina tambayarku, ‘Waceƙara kuke da ita game da ni?’Kun yi mini tawaye dukanku.
30. Na hori 'ya'yanku, amma a banza, basu horu ba,Kun kashe annabawanku da takobikamar mayunwacin zaki.
31. Ya ku mutanen zamanin nan, kusaurari maganata.Na zamar wa Isra'ila jeji? Ko ƙasarda take da kurama?Don me fa mutanena suke cewa,‘Mu 'yantattu ne,Ba za mu ƙara zuwa wurinka ba’?
32. Budurwa ta manta da kayankwalliyarta?Ko kuwa amarya ta manta da kayanadonta?Amma mutanena sun manta da nikwanaki ba iyaka.
33. Kun sani sarai yadda za ku yi kufarauci masoya,Har mugayen mata ma, kun koyamusu hanyoyinku.