25. “Kai kuma, Ezra, bisa ga hikimar da Allahnka ya ba ka, sai ka naɗa mahukunta da alƙalai waɗanda za su yi wa mutanen da suke a lardin Yammacin Kogi shari'a, wato dukan waɗanda suka san shari'a. Waɗanda ba su san shari'a ba kuwa, sai ka koya musu.
26. Duk wanda bai yi biyayya da shari'ar Allahnka ba, ko shari'ar sarki, sai a yi masa hukunci mai tsanani, ko na mutuwa, ko na kora, ko na ƙwace dukiyarsa, ko na kurkuku.”
27. Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na kakanninmu, wanda ya sa a zuciyar sarki ya ƙawata Haikalin Ubangijin da yake a Urushalima.
28. Wanda kuma ya sa na sami tagomashi a wurin sarki, da 'yan majalisarsa, da manyan ma'aikatansa. Na sami ƙarfin hali, gama Ubangiji Allahna yana tare da ni. Sai na tattara manyan mutane na Isra'ila don mu tafi tare.