5. Ka kama mafi kyau daga cikin garken,Ka sa sauran ƙasusuwa a ƙarƙashinsa,Ka tafasa gunduwoyin,Ka kuma tafasa tantakwashin.’
6. “Ni Ubangiji Allah na ce,‘Domin haka kaiton birnin nan mai zubar da jini,Da tukunya wadda take da tsatsa,Wadda tsatsarta ba ta fita cikinta ba!Ka sa sauran ƙasusuwa a ƙarƙashinsa,Kada ka yi zaɓe.
7. Gama jinin da ta zubar yana tsakiyarta,Ta zubar da shi a kan dutse,Ba ta zubar da shi a ƙasa inda za ta rufe shi da ƙura ba.