Ez 21:9-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

9. “Ya ɗan mutum, ka yi annabci, ka ce ni Ubangiji na ce,‘Takobi, takobi wasasshe,Kuma gogagge!

10. An wasa shi domin kisa,An goge shi don ya yi walwal kamar walƙiya!’Ba wanda zai iya tsai da shi, domin kun ƙi karɓar shawara.

11. An ba da takobin a goge shi domin a riƙe. An wasa shi, an kuma goge shi domin a ba mai kashewa.

12. Ka yi kuka, ka yi ihu, ya ɗan mutum, gama takobin yana gāba da jama'ata da dukan shugabannin Isra'ila. An ba da shugabanni da jama'ata ga takobi, sai ka buga ƙirjinka da baƙin ciki.

13. Gama ba don jarraba shi ba ne, sai me kuma idan ka raina sandan? Ni Ubangiji na faɗa.

14. “Domin haka, ya kai ɗan mutum, ka yi annabci, ka tafa hannuwanka, ka kaɗa takobi sau biyu, har sau uku. Takobin zai kashe waɗanda za a kashe. Takobi ne na yin kashe-kashe mai yawa. Zai kewaye su.

15. Zai sa zukatansu su narke, da yawa kuma su fāɗi a ƙofofinsu. Na ba da takobi mai walƙiya. An yi shi kamar walƙiya, an wasa shi don kashe-kashe.

16. Ka yi sara dama da hagu, duk inda ka juya.

17. Ni kuma zan tafa hannuwana, zan aukar da fushina, ni Ubangiji na faɗa.”

18. Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce,

19. “Ya ɗan mutum, ka nuna hanya biyu inda takobin Sarkin Babila zai bi. Dukansu biyu za su fito daga ƙasa ɗaya. Ka kafa shaidar hanya a kan magamin hanya zuwa birni.

20. Ka nuna wa takobin hanya zuwa Rabba ta Ammonawa, da hanya zuwa Yahuza, da Urushalima, birni mai garu.

21. Gama Sarkin Babila yana tsaye a mararrabar hanya, inda hanyar ta rabu biyu, yana yin dūbā, yana girgiza kibau, yana neman shawara wurin kan gida, yana dūbān hanta.

Ez 21