Ez 10:17-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Sa'ad da suka tsaya cik, sai ƙafafun su ma su tsaya cik, sa'ad da suka tashi sama, sai su kuma su tashi tare da su, gama ruhun talikan yana cikinsu.

18. Sai ɗaukakar Ubangiji ta tashi daga bakin ƙofar Haikalin, ta tsaya bisa kerubobin.

19. Kerubobin kuwa suka ɗaga fikafikansu, suka tashi daga ƙasa, suka yi sama a kan idona, suka tafi da ƙafafun gab da su. Suka tsaya a ƙofar gabas ta Haikalin Ubangiji. Ɗaukakar Allah na Isra'ila kuwa tana bisa kansu.

20. Waɗannan su ne talikan da na gani a ƙarƙarshin kursiyin Allah na Isra'ila a bakin kogin Kebar, na kuwa sani su kerubobi ne.

21. Kowannensu yana da fuska huɗu, da fiffike huɗu. A ƙarƙashin fikafikansu suna da hannuwa irin na 'yan adam.

22. Kamannin fuskokinsu kuma daidai yake da kamannin fuskokin da na gani a bakin kogin Kebar. Sai suka tafi, kowa ya nufi gabansa sosai.

Ez 10