26. Ina umartar mutanen da suke cikin mulkina su yi rawar jiki, su ji tsoron Allah na Daniyel,Gama shi Allah ne mai rai, Madawwami,Sarautarsa ba ta tuɓuwa,Mulkinsa kuma madawwami ne.
27. Yakan yi ceto, yakan kuma kuɓutar,Yana aikata alamu da mu'ujizai a sama da duniya.Shi ne wanda ya ceci Daniyel daga bakin zakoki.”
28. Daniyel kuwa ya bunƙasa a zamanin mulkin Dariyus da na Sairus mutumin Farisa.