18. Nan take sai wani abu kamar ɓawo ya faɗo daga idanunsa, sai ya sāke gani. Sa'an nan ya tashi, aka yi masa baftisma.
19. Sai ya ci abinci, ƙarfinsa kuma ya komo.Shawulu kuwa ya yi 'yan kwanaki tare da masu bi da suke Dimashƙu.
20. Nan da nan ya fara wa'azin Yesu a majami'unsu, cewa shi ne Ɗan Allah.
21. Duk waɗanda suka ji shi, suka yi ta al'ajabi, suka ce, “Ashe, ba wannan ne ya watsa masu yin addu'a da sunan nan a Urushalima ba? Ya zo nan ne ma da niyyar ya kai su gaban manyan firistoci a ɗaure.”