5. Filibus ya tafi birnin Samariya, yana ta yi musu wa'azin Almasihu.
6. Da taron suka ji, suka kuma ga mu'ujizan da Filibus yake yi, da nufi ɗaya suka mai da hankali ga abin da ya faɗa.
7. Domin da yawa masu baƙaƙen aljannu suka rabu da su, aljannun kuwa na ta ihu. Shanyayyu da guragu da yawa kuma an warkar da su.
8. Saboda haka aka yi ta farin ciki a garin ƙwarai da gaske.
9. Akwai wani mutum kuwa, mai suna Saminu, wanda dā yake sihiri a birnin, har yana ba Samariyawa mamaki, yana cewa shi wani muhimmi ne.
10. Duk jama'a kuwa suka mai da hankali a gare shi, babba da yaro, suna cewa, “Mutumin nan, ai, ikon nan ne na Allah, da ake kira mai girma.”