18. Sarki kuwa ya ce, “A bar shi yadda yake, kada wani ya taɓa ƙasusuwansa.”Sai suka bar ƙasusuwan annabin da ya zo daga Samariya.
19. Dukan matsafai na kan tuddai da suke a garuruwan Samariya waɗanda sarakunan Isra'ila suka gina, har suka sa Ubangiji ya yi fushi, Yosiya ya watsar da su. Ya yi da su kamar yadda ya yi a Betel.
20. Ya kuma karkashe dukan firistocin matsafai na kan tuddai a bisa bagadan da suke can. Ya ƙone ƙasusuwansu a bisa bagadan. Sa'an nan ya komo Urushalima.
21. Sarki Yosiya kuwa ya umarci dukan mutane, ya ce, “Ku kiyaye Idin Ƙetarewa ga Ubangiji Allahnku kamar yadda aka rubuta a littafin alkawari.”
22. Gama ba a ƙara kiyaye Idin Ƙetarewa ba tun daga zamanin hakimai waɗanda suka yi hukuncin Isra'ila, ko a zamanin sarakunan Isra'ila da na Yahuza,