2 Sam 20:17-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Da ya zo kusa da ita, sai macen ta ce, “Kai ne Yowab?”Ya ce, “I, ni ne.”Ta ce masa, “Ka kasa kunne gare ni.”Ya ce, “Ina sauraronki.”

18. Ta ce, “A dā sukan ce, ‘A nemi shawara a Abel,’ gama a can ake raba gardama.

19. Garinmu lafiyayye ne, amintacce ne kuma a cikin Isra'ila. Me ya sa kake so ka hallaka garin? Kana so ka rushe abin da yake na Allah?”

20. Yowab ya ce, “Allah ya sawwaƙe! Ba zan lalatar ko in hallakar da birninku ba.

21. Ba haka ba ne, ni dai ina neman mutumin ƙasar tudu ta Ifraimu, wanda ake ce da shi Sheba, ɗan Bikri. Shi ne ya tayar wa sarki Dawuda. Shi kaɗai za ku ba ni, ni kuwa zan janye daga garin.”Macen kuwa ta ce wa Yowab, “To, za a jefar maka kansa ta kan garu.”

2 Sam 20