31. Waɗannan su ne waɗanda Dawuda ya sa su su zama mawaƙa a Haikalin Ubangiji, sa'ad da aka kawo akwatin alkawari a cikin Haikalin.
32. Suka yi ta raira waƙoƙi a gaban wurin zama na alfarwa ta taruwa tun kafin Sulemanu ya gina Haikalin Ubangiji a Urushalima. Suka yi hidima bisa ga matsayinsu ta yadda aka tsara.
33. Waɗannan su ne waɗanda suka yi ta raira waƙoƙin, su da 'ya'yansu maza.Daga iyalin Kohat, Heman shi ne shugaban ƙungiyar farko ta mawaƙa, shi ɗan Yowel ne, ɗan Sama'ila,
34. ɗan Elkana, ɗan Yeroham, ɗan Eliyab, ɗan Mahat,
35. ɗan Zafai, ɗan Elkana, ɗan Mahat, ɗan Amasai,
36. ɗan Elkana, ɗan Shawul, ɗan Azariya, ɗan Uriyel,
37. ɗan Tahat, ɗan Assir, ɗan Ebiyasaf, ɗan Kora,
38. ɗan Izhara, ɗan Kohat, ɗan Lawi, ɗan Isra'ila.
39. Asaf kuma shi ne shugaban ƙungiyar mawaƙa ta biyu. Shi ɗan Berikiya ne, ɗan Shimeya,
40. ɗan Maikel, ɗan Ba'aseya, ɗan Malkiya,
41. ɗan Yewaterai, ɗan Zera, ɗan Iddo,
42. ɗan Yowa, ɗan Zimma, ɗan Shimai,
43. ɗan Yahat, ɗan Gershon, ɗan Lawi.
44. Etan na zuriyar Merari, shi ne shugaban ƙungiyar mawaƙa ta uku, asalinsa shi ɗan Kishi ne, ɗan Abdi, ɗan Malluki,
45. ɗan Hashabiya, ɗan Amaziya, ɗan Hilkiya,
46. ɗan Amzi, ɗan Bani, ɗan Shemer,
47. ɗan Mali, ɗan Mushi, ɗan Merari, ɗan Lawi.
48. Aka sa 'yan'uwansu, Lawiyawa, su yi dukan hidimomi a cikin Haikalin Ubangiji.
49. Amma Haruna da 'ya'yansa maza suka miƙa hadayu a kan bagaden hadaya ta ƙonawa, da kan bagaden ƙona turare, domin dukan aikin Wuri Mafi Tsarki, da kuma yin kafara domin Isra'ila bisa ga dukan abin da Musa, bawan Allah, ya umarta.