1 Sam 2:3-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Kada ku ƙara yin magana ta girmankai,Ku daina maganganunku na fariya,Gama Ubangiji Allah shi ne masani,Yana kuma auna dukkan aikin da mutum ya yi.

4. An kakkarya bakunan ƙarfafan sojoji,Amma rarrauna ya zama mai ƙarfi.

5. Ƙosassun mutane suna ƙodago saboda abinci,Masu fama da yunwa kuwa sun daina jin yunwa.Bakarariya ta haifi 'ya'ya bakwai,Wadda ta haifi 'ya'ya da yawa kuwata rasa su duka.

6. Ubangiji ne yake kashewa, ya kuma rayar,Yana kai mutane kabari,Ya kuma tā da su.

1 Sam 2