1 Sam 2:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Hannatu kuwa ta yi addu'a ta ce,“Ubangiji ya cika zuciyata da murna.Ina farin ciki da abin da ya yi.Ina yi wa maƙiyana dariya,Ina matuƙar murna domin Allah ya taimake ni.

2. “Babu wani mai tsarki kamar Ubangiji,Babu wani mai kama da shi,Ba mai kiyaye mu kamar Allahnmu.

3. Kada ku ƙara yin magana ta girmankai,Ku daina maganganunku na fariya,Gama Ubangiji Allah shi ne masani,Yana kuma auna dukkan aikin da mutum ya yi.

4. An kakkarya bakunan ƙarfafan sojoji,Amma rarrauna ya zama mai ƙarfi.

1 Sam 2