Zab 72:5-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Ka sa su girmama kaMuddin rana tana haskakawa,Muddin wata yana ba da haske dukan lokaci.

6. Ka sa sarki ya zama kamar ruwan sama a gonaki,Ya zama kamar yayyafi a bisa ƙasa.

7. Ka sa adalci ya bunƙasa a zamaninsa,Wadata ta dawwama muddin wata na haskakawa.

8. Mulkinsa ya kai daga teku zuwa teku,Daga Kogin Yufiretis, har zuwa iyakar duniya.

9. Kabilan hamada za su durƙusa a gabansa,Abokan gābansa za su kwanta warwar a cikin ƙura.

10. Sarakunan Esbanya da na tsibirai,Za su ba shi kyautai,Sarakunan Arabiya da na HabashaZa su kawo masa kyautai.

11. Dukan sarakuna za su durƙusa a gabansa,Dukan sauran al'umma za su bauta masa!

12. Yakan ceci matalauta waɗanda suka yi kira gare shi,Da waɗanda suke da bukata,Da waɗanda ba a kula da su.

13. Yakan ji tausayin gajiyayyu da matalauta,Yakan ceci rayukan waɗanda suke da bukata.

Zab 72