Zab 68:3-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Amma adalai za su yi murna,Su kuma yi farin ciki a gaban Allah,Za su yi murna ƙwarai da gaske.

4. Ku raira waƙa ga Allah,Ku raira waƙar yabo ga sunansa,Ku yi hanya ga wanda yake ratsa gizagizai.Sunansa kuwa Ubangiji ne, ku yi murna a gabansa!

5. Allah, wanda yake zaune a tsattsarkan Haikalinsa,Yana lura da marayu, yana kuwa kiyaye gwauraye,Wato matan da mazansu suka mutu.

Zab 68