1. Ya Allah, dole mutane su yabe ka a Sihiyona,Tilas su ba ka abin da suka alkawarta.
2. Saboda kakan amsa addu'o'i,Dukan mutane za su zo wurinka.
3. Zunubanmu sun kāshe mu,Amma za ka gafarta zunubanmu.
4. Masu farin ciki ne waɗanda ka zaɓe suSu zauna a tsattsarkan wurinka!Za mu ƙoshi da kyawawan abubuwa da suke wurin zamanka,Da albarkun tsattsarkan Haikalinka!