15. Ka ga lokacin da ƙasusuwana suke siffatuwa,Sa'ad da kuma ake harhaɗa su a hankaliA cikin mahaifiyata,Lokacin da nake girma a asirce.
16. Ka gan ni kafin a haife ni.Ka ƙididdige kwanakin da ka ƙaddara mini,Duka an rubuta su a littafinka,Tun kafin faruwar kowannensu.
17. Ya Allah, tunaninka suna da wuyar ganewa a gare ni,Ba su da iyaka!
18. In na ƙirga su, za su fi tsabar yashi,Sa'ad da na farka, har yanzu ina tare da kai.
19. Ya Allah, da yadda nake so ne, da sai ka karkashe mugaye!'Yan ta da zaune tsaye kuma sai su rabu da ni!