12. Amma har duhun ma, ba duhu ba ne a gare ka,Dare kuwa haskensa kamar na rana ne.Duhu da haske, duk ɗaya ne gare ka.
13. Kai ne ka halicci kowace gaɓa ta jikina,Kai ne ka harhaɗa ni a cikin mahaifiyata.
14. Ina yabonka gama kai abin tsoro ne,Dukan abin da ka yi sabo ne, mai banmamaki.Da zuciya ɗaya na san haka ne.