3. Yana kama da itacen da yake a gefen ƙorama,Yakan ba da 'ya'ya a kan kari,Ganyayensa ba sa yin yaushi,Yakan yi nasara a dukan abin da yake yi.
4. Amma mugaye ba haka suke ba,Su kamar yayi suke wanda iska take kwashewa.
5. Allah kuwa zai hukunta mugaye,Masu zunubi kuwa za a ware su daga adalai.
6. Gama Ubangiji yana lura da al'amuran adalai,Amma al'amuran mugaye za su watse.