1. Ifraimu tana kiwon iska,Tana ta bin iskar gabas dukan yini.Tana riɓaɓɓanya ƙarya da kamakarya.Tana ƙulla yarjejeniya da Assuriya,Tana kai mai a Masar.”
2. Ubangiji yana da magana game da mutanen Yahuza,Zai hukunta Isra'ila saboda hanyoyinta,Zai sāka mata gwargwadon ayyukanta.