1. Ku busa ƙaho, ku yi gangami,A cikin Sihiyona, tsattsarkandutsen Allah!Duk mutanen ƙasar za su yi rawarjiki,Domin ranar Ubangiji tana zuwa, tayi kusa.
2. Za ta zama rana ce mai duhudulum,Ranar gizagizai ce baƙi ƙirin.Runduna mai ƙarfi tana tasowa,Kamar ketowar hasken safiya bisatsaunuka.Faufau ba a taɓa ganin irinta ba,Ba kuwa za a sāke ganin irinta ba.
3. Tana cinye shuke-shuke kamar wuta,Ƙasa kamar gonar Adnin take kafinta zo,Amma a bayanta ta zama hamada,Ba abin da ya tsere mata.