4. Bayan ya fitar da dukan nasa waje, sai ya shige gabansu, tumakin na biye da shi, domin sun san murya tasa.
5. Ba za su bi baƙo ba, sai dai su guje shi, don ba su san muryar baƙo ba.”
6. Yesu ya yi musu wannan misali, amma ba su gane abin da ya faɗa musu ba.
7. Don haka Yesu ya sāke ce musu, “Lalle hakika, ina gaya muku, ni ne ƙofar tumakin.