26. Ta haka nan ne Isra'ila duka za su sami ceto, kamar yadda yake a rubuce cewa,“Mai Ceto zai zo daga Sihiyona,Zai kuma kawar da rashin bin Allah daga zuriyar Yakubu,”
27. “Cikar alkawarina a gare su ke nan,Sa'ad da na ɗauke musu zunubansu.”
28. A game da bishara kuma, maƙiyan Allah ne su, domin amfaninku ne kuwa. Amma a game da zaɓen Allah, su ƙaunatattunsa ne, albarkacin kakannin kakanninsu.
29. Domin baiwar Allah da kiransa ba sa tashi.
30. Kamar yadda kuka ƙi bin Allah a dā, amma a yanzu aka yi muku jinƙai saboda rashin biyayyarsu,
31. haka su ma da suke marasa biyayya a yanzu, yanzu a yi musu jinƙai kamar yadda aka yi muku.
32. Don Allah ya kulle kowa a cikin rashin biyayya, domin ya nuna jinƙai ga kowa.
33. Zurfin hikimar Allah da na saninsa da rashin iyaka suke! Hukunce-hukuncensa sun fi gaban bincikewa, hanyoyinsa kuma sun fi gaban bin diddigi!