3. Sa'an nan na ce musu, kada su buɗe ƙofofin Urushalima da sassafe, sai rana ta cira sosai, su kuma kulle ƙofofin da ƙarfe kafin matsara su tashi wajen faɗuwar rana. Su samo matsara daga mazaunan Urushalima, su sa su tsaye a muhimman wurare, waɗansunsu kuma suna zaga gidaje.
39-42. Ga lissafin iyalin firistoci da suka komo daga zaman talala.Yedaiya, na zuriyar Yeshuwa, ɗari tara da saba'in da ukuImmer, dubu ɗaya da hamsin da biyu (1,052)Fashur, dubu da ɗari biyu da arba'in da bakwai (1,247)Harim, dubu ɗaya da goma sha bakwai (1,017)