1. “Ku yi hankali kada ibadarku ta zama ta ganin ido. Domin in kun yi haka, ba za ku sami sakamako wurin Ubanku da yake a Sama ba.
2. “Wato, in za ka yi sadaka, kada ka yi kwakwazo yadda munafukai suke yi a majami'u da kuma kan hanya don dai mutane su yabe su. Gaskiya nake faɗa muku, sun sami iyakar ladarsu ke nan.
3. Amma in kana yin sadaka, kada hannunka na hagu ya san abin da hannunka na dama yake yi,
4. domin sadakarka tă zama a asirce, Ubanku kuwa da yake ganin abin da ake yi a asirce, zai sāka maka.”
5. “In za ku yi addu'a, kada ku zama kamar munafukai, don sun cika son yin addu'a a tsaye a majami'u da kan hanya, wai mutane su gan su. Gaskiya nake gaya muku, sun sami iyakar ladansu.
6. Amma in za ka yi addu'a, sai ka shiga lollokinka, ka rufe ƙofa, ka yi addu'a ga Ubanku wanda yake ɓoye, Ubanku kuwa da yake ganin abin da ake yi a asirce, zai sāka maka.
7. “In kuwa kuna addu'a, kada ku yi ta maimaitawar banza, kamar yadda al'ummai suke yi, a zatonsu za a saurare su saboda yawan maganarsu.
8. Kada ku zama kamarsu, domin Ubanku ya san bukatarku tun kafin ku roƙe shi.
9. Saboda haka sai ku yi addu'a kamar haka,‘Ya Ubanmu, wanda yake cikin Sama,A kiyaye sunanka da tsarki.
10. Mulkinka yă zo,A aikata nufinka a duniya kamar yadda ake yi a Sama.
11. Ka ba mu abincinmu na yau.
12. Ka gafarta mana laifofinmu,Kamar yadda mu ma muke gafarta wa waɗanda suke yi mana laifi.
13. Kada ka kai mu wurin jaraba,Amma ka cece mu daga Mugun.’
14. Domin in kun yafe wa mutane laifofinsu, Ubanku na Sama zai yafe muku.
15. In kuwa ba ku yafe wa mutane laifofinsu ba, Ubanku ma ba zai yafe muku naku ba.”
16. “In kuma kuna yin azumi, kada ku turɓune fuska kamar munafukai, don sukan yanƙwane fuska, wai don mutane su ga suna azumi ne. Hakika, ina gaya muku, sun sami iyakar ladansu ke nan.
17. Amma in kana azumi, ka shafa mai a ka, ka kuma wanke fuska,