Mat 20:6-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Wajen la'asar kuma ya fita ya sami waɗansu a tsaitsaye, ya ce musu, ‘Don me kuke zaman banza yini zubur?’

7. Sai suka ce masa, ‘Don ba wanda ya ɗauke mu aiki.’ Ya ce musu, ‘Ku ma ku tafi garkata.’

8. Da magariba ta yi, mai garkar inabin ya ce wa wakilinsa, ‘Kirawo ma'aikatan, ka biya su hakkinsu, ka fara daga na ƙarshe har zuwa na farko.’

9. Da waɗanda aka ɗauka wajen la'asar suka zo, sai ko wannensu ya sami dinari guda.

Mat 20