24. Da ya fara ƙididdigar, sai aka kawo masa wanda yake bi talanti dubu goma bashi.
25. Da yake ya gagara biya, sai ubangidansa ya yi umarni a sayar da shi da mata tasa da 'ya'yansa da kuma duk abin da ya mallaka, a biya kuɗin.
26. Sai bawan ya faɗi a gabansa ya yi masa ladabi, ya ce, ‘Ya ubangida, ka yi mini haƙuri, zan biya ka tsaf.’
27. Saboda tausayin bawan nan ubangidansa ya sake shi, ya yafe masa bashin.