Mat 18:24-27 Littafi Mai Tsarki (HAU)

24. Da ya fara ƙididdigar, sai aka kawo masa wanda yake bi talanti dubu goma bashi.

25. Da yake ya gagara biya, sai ubangidansa ya yi umarni a sayar da shi da mata tasa da 'ya'yansa da kuma duk abin da ya mallaka, a biya kuɗin.

26. Sai bawan ya faɗi a gabansa ya yi masa ladabi, ya ce, ‘Ya ubangida, ka yi mini haƙuri, zan biya ka tsaf.’

27. Saboda tausayin bawan nan ubangidansa ya sake shi, ya yafe masa bashin.

Mat 18